Header Ads Widget

 


Ma'aikatan jinya a Najeriya sun sanar da janye yajin aiki


Babbar ƙungiyar ma'aikatan jinya da ungozoma a Najeriya ta sanar da janye yajin aiki na kwana bakwai da ta fara yi bayan cimma matsaya da gwamnatin tarayya.

Sun fara yajin ne a ranar Laraba bayan sun zargi gwamnatin ƙasar da kasa cika alƙawarin ƙara musu albashi da alawus-alawus, da ƙara yawan ma'aikata, da inganta wuraren aiki.

Shugaban ƙungiyar ta National Association of Nigeria Nurses and Midwives (NANNM), Haruna Mamman, ya shaida wa BBC cewa gwamnati ta bayar da umarnin cika akasarin buƙatun nasu.

"Saboda yarjejeniyar da muka cimma da kuma nuna jajircewarmu, mun jingine yajin aikin da muke yi na ƙasa baki ɗaya nan take," in ji shi cikin wata sanarwa daban a yau Asabar.

A jiya Juma'a Ministan Lafiya na Najeriya Muhammed Ali Pate ya ce ƙungiyar ta amince da janye yajin aikin bayan yarjejeniyar da suka ƙulla.

Sanarwar ta nemi 'ya'yan ƙungiyar su koma bakin aikinsu nan take.

Post a Comment

0 Comments