Daga Hassan Ibrahim
Zaɓaɓɓen ɗan takarar jam'iyyar PDP
na mazaɓar Zaria Kewaye a zaɓen fidda gwani da ya gabata, Alhaji Abdullahi
Mamuda Wappah ya miƙa godiya ga Allah SWT da ya nuna masa wannan rana da kuma
ya bashi nasara a zaɓen da ya gabata.
Ya yi godiya ta musamman ga shuwagabannin
jam'iyya na PDP tun daga matakin jiha, Ƙananan hukumomi zuwa Mazaɓu ,da Deliget da suka gudanar da zaɓen.
“Kasancewar Nasara daga Allah ne
kuma naji daɗi da ya ba ni wannan Nasara,babban fata na shine Allah ya bani Nasara a zabe mai zuwa”, Inji
shi.
Abdullahi ya kuma godewa al'umma waɗanda
suka yi masa fatan alkhairi da adduo'i dan samun nasara, babu abinda zance sai
dai in ce Allah ya saka musu da alkhairi.
Ya kuma ƙara da cewa, su kuma
abokanan takara na, ina yi musu fatan alkhairi kuma ina neman shawarwari daga
gare su domin tunkarar zaɓe na gaba.
Ina kira ga al'umma da su fito ranar
16 ga watan Augusta, shekara ta 2025, dan ganin sun mara mana baya domin kaiwa
ga gaci.
“Yanda nike matashi ina so matasa su
bani goyon baya mu ci wannan zabe, su gujewa duk wani abu da ka iya tayar da
zaune tsaye lokacin zaben”, a cewar sa.
Ya kuma yi addu'ar samun dawwamammen
zaman lafiya ƙaruwar arziki da ci gaba mai ɗorewa a masarautar Zazzau, jihar
Kaduna da ma Nijeriya baki daya.
Usman Jibril wanda aka fi sani da
Rubuci, babban Darakta na tafiyar ɗan takarar yace abin godiya ne ga Allah SWT
yanda aka gudanar da zaɓen cikin lafiya da kwanciyar hankali.
Kazalika ya mika godiya da jinjina
ga Delegates, masu ruwa da tsaki, shuwagabannin jam'iyya na PDP tun daga
matakin jiha zuwa ƙananan Hukumomi da Mazaɓu, yanda suka bada goyon baya dan
ganin wannan zaɓe ya tabbata cikin lafiya da kwanciyar hankali.
Daga ƙarshe, ya yi kira ga sauran
abokan takara da su zo a haɗa hannu a matsayin ƴan ƙaramar hukumar Zaria dan
fitar da kitse a wuta na baiwa jam'iyyar PDP goyon baya kasancewar za'a samu
canji na gari.


0 Comments