Header Ads Widget

 


Sheikh Usman Idris Kusfa Ya Rasu Bayan Ya Yi Doguwar Jinya


Daga Hassan Ibrahim 

Allah ya yi wa fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Usman Idris Kusfa Zaria (Rigi-Rigi) rasuwa, bayan ya sha fama da jinya.

Marigayin ya rasu ne a wani asibiti da ke cikin garin Kaduna a safiyar ranar Litinin.

Rahotanni sun bayyana cewa za a gudanar da sallar jana’izarsa a yau Litinin da misalin ʙarfe 4:30 na yamma, a Kusfa da ke Zariya.

Sheikh Usman Idris ya rasu yana da shekaru 56 a duniya, ya bar mata huɗu da ’ya’ya 37, kamar yadda Sagir ɗan Sardauna ya shaida wa Daily Naija Updates.

Muna roʙon Allah Maɗaukakin Sarki ya jikansa, ya gafarta masa kurakuransa, ya kuma sanya Aljannah Firdausi ta zama makomarsa, Aameen.


Post a Comment

0 Comments