Header Ads Widget

 


Jaridar Taskira Ta Karrama Barrister Aisha Iyal Waziri Bisa Kwarewa da Rikon Amana a Aikinta


Daga Hassan Ibrahim 


Jaridar Taskira ta karrama Barrister Aisha Iyal Waziri a ranar Lahadi, 21 ga watan Yuni, 2026, bisa jajircewarta wajen gudanar da aikinta tare da gudummawar da take bayarwa ga al’umma ta fuskar hidimar shari’a da gudanarwa.

Barrister Aisha Iyal Waziri, wadda ke aiki a matsayin Magatakardar Upper Sharia Court III, ta bayyana farin cikinta da godiyarta ga Allah Madaukakin Sarki bisa damar da ta samu na karɓar wannan lambar yabo, tare da miʙa godiya ga Jaridar Taskira saboda ganin ta cancanci wannan girmamawa.

Ta bayyana cewa samun irin wannan karramawa bisa cancanta yana da matuʙar muhimmanci ga duk wani ma’aikaci, domin yana ʙara masa ʙwarin gwiwa wajen ci gaba da gudanar da aikinsa cikin gaskiya, riʙon amana da kuma tsoron Allah.

Barrister Aisha ta jaddada cewa ita da abokan aikinta suna ʙoʙarin ganin an tabbatar da tsafta da inganci a harkokin aiki, tana mai cewa da taimakon Allah suna yin iya ʙoʙarinsu wajen sauke nauyin da aka ɗora musu yadda ya kamata.

Ta kuma bayyana cewa tana yawan bai wa ma’aikatan da suka yi aiki tare da ita shawara da su kasance masu haʙuri, lura da ʙananan bayanai da kuma mai da hankali ga abubuwan da suka shafi aikin kotu, domin waɗannan su ne ginshiʙan nasara a aikin shari’a da gudanarwa.

A cewarta, abin da ta fi so shi ne ganin ma’aikaci ya tsaya tsayin daka wajen gudanar da aikinsa cikin ʙwazo da gaskiya tare da tabbatar da adalci ga al’umma.
Ta ʙara da cewa tsoron Allah shi ne mataki na farko na nasara ga kowane ma’aikaci, yayin da jajircewa da riʙon amana suke zama tubalan ci gaba da ɗaukaka a rayuwa da kuma a wurin aiki.

“Tsoron Allah da jajircewa a aiki su ne manyan saʙonnin da nake son isarwa ga kowane ma’aikaci,” in ji Barrister Aisha Iyal Waziri.





Post a Comment

0 Comments